Allah Ya karbi ran tsohon Shugaban majalisar dokokin jihar Katsina Kabir Ahmad Kofa bayan fama da rashin lafiya.
Kabir Ahmad Kofa ya rasu ne a daren Asabar wayewar Lahadi a wani asibiti dake a cikin birnin Katsina.
Kabir Ahmad Kofa ne shugaban majalisar dokokin jihar Katsina daga shekarar 1999 zuwa 2007, daga nan ya zama dan majalisar wakilan Nijeriya a shekarar 2007 zuwa 2011 duk a jam’iyyar PDP.
Bayanai sun ce za a gabatar da jana’izarsa da misalin karfe goma na safiyar Lahadin nan a masallacin GRA Katsina.